Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un! Allah ya yiwa shahrarren mawakin Hausa, Hassan Wayam rasuwa.
Wayan ya rasu ne yana mai shekaru 64 a daren Juma'a a asibiti bayan dogon jinyan da yayi fama da shi, cewar majiyoyi.
Hassan Wayam wanda aka haifa 1956 a kauyen Gwadda dake karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara, ya fara waka ne a garin Mayanci sannan ya koma Zariya a 1969, Daily Nigerian ta ruwaito.
Ya shahara a Arewacin Najeriya inda yake waka a taruka.
Wakokinsa mafi shahara sun hada da “Tana Kukan Kurciya”, “Ba Ni Ne Na Fada Ba, Hassan Wayam Ne Ya Fada”, “Kowac Ci Kurciya”, da sauransu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng
ncG1vNJzZmigkarAonrLnp6irF6jtHB9knBubmxlYq6tuMChZLKZXa62uK2MrJ%2BaoKKWv7OxzWakmq%2BRoLZutMCsqpqmXayuuq3MZqmaq6Wsrm%2B006aj